Yan tawaye sun kai hari kan soji a Kongo
November 25, 2006Talla
A kasar Kongo magoya bayan wani janar na soja da yayi tawaye sun kai hari da manyan makamai kan sansanonin soji a gabashin kasar.
Ministan harkokin cikin gida na Kongo Denis Kalume yace dakarun shugaban tawayen janar Laurent Nkunda sun kaddamar da hari a sansanin Sake yau da safen nan,inda dakarun sojin kasar kuma suka maida martani.
Majiyoyi daga MDD sun tabbatar da kaiwa wannan hari a yankin na Sake wanda shinnge ne tsakanin dakarun gwamnati dana yan tawayen.