1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yan tawaye sun kai hari a ƙasar Mali

May 11, 2007
https://p.dw.com/p/BuLd

Rahottani daga ƙasar Mali, sun ce wani ayarin abzinawa ɗauke da makamai, da su ka zo daga Jamhuriya Niger, da Mali, sun kai hari ga cibiyar jami´an tsaro, da ke Tinza, a yankin Kidal, kussa da iyaka da Algeria.

Wannan shine hari mafi girma da abizanawa yan tawaye su ka kai, a ƙasar tun bayan yarjejniyar sulhu da aka rattaba hannu kan ta, a ƙasar Algeria ranar 4 ga watan juli na shekara da ta gabata.

Ƙungiyar tawayen da Ibrahim Bahanga ke jagoranta, ta ɗauki alhakin kai wannan hari, wanda ya zuwa yanzu, a ba tantance sakamakon assara da ya jawo ba.

Saidai gwamantin Bamako, ta tura ƙarin jami´n tsaro, a yankin da abunya faru.

Ƙasar Mali, na ɗaya daga ƙasashen Afrika kudanci Sahara da ke fama da rikicin tawaye.