1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan Taliban sun kai wani hari a Kabul

Zulaiha Abubakar
March 1, 2017

Kungiyoyin 'yan ta'addan sun zafafa hare-haren da suke kai kwanakinnan a kasar ta Afganistan abin da ke maida agogo baya bisa shirin zamar da zaman lafiya mai dorewa a kasar.

https://p.dw.com/p/2YShj
Afghanistan Anschlag in Kabul
Hoto: Reuters/M. Ismail

Harin dai ya yi sandiyyar rasa rayuka da kuma jikkata mutane 38, tun da farko dai wasu 'yan kunar bakin wake ne suka afka da mota cikin wani sansani na jami'an tsaro, inda suka dinga musayar wuta a tsakanin su, a daidai lokacin da bom ya tashi da wani dan ta'adda da ke kokarin shiga ofishin leken asiri a gabashin Kabul, babban birnin kasar ta Afganistan. Ya zuwa yanzu dai kakakin kungiyar ta Taliban Zabihullah Mujahid, ya rubuta a shafin twitter cewar 'yan kungiyar su ne suka kai harin kuma sun yi shahada.