1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan ta'adda sun kashe sojoji Nijar 23 a yakin Tillaberi

Mouhamadou Awal Balarabe
March 22, 2024

Gwamnatin sojan Nijar ta ce kwantan bauna da masu ikirarin jihadi suka kai a kusa da iyakar kasar da Burkina Faso da Mali ne ya yi sanadin mutuwar dakarunta. Amma sojojin sun yi nasarar kame 'yan ta'adda kusan talatin,

https://p.dw.com/p/4e10x
Sojojin Nijar na tinkarar 'yan ta'adda gadan-gadan
Sojojin Nijar na tinkarar 'yan ta'adda gadan-gadanHoto: Mads Claus Rasmussen/Ritzau Scanpix/picture alliance

Gwamnatin mulkin sojan Nijar ta sanar da mutuwar dakarunta 23 a kwantan bauna da masu ikirarin jihadi suka kai a yankin da ke kusa da iyakar kasar da Burkina Faso da Mali. Wannan sabon harin ya faru ne a lokacin da sojojin ke sintiri a cikin wannan mako don dakile ayyukan ta'addanci a yankin Tillabéri, wanda ya ba su damar kame 'yan ta'adda kusan talatin, a cewar sanarwar da ma'aikatar tsaro ta fitar a birnin Yamai.

karin bayani:Matsalolin tsaro bayan juyin mulki a Nijar

Tun shekarun bakwai da suke gabata ne yankin Tillabery ya zama maboyar masu ikirarin jihadi ciki har da Al Qaeda, inda ake fama da hare-haren kungiyoyi da ke dauke da makamai, duk da dimbin dakarun da ke jibge a wannan yanki. Ko da a karshen watan Janairu, an kashe fararen hula 22 a wani hari da aka kai a kauyen Motogatta da ke cikin gundumar Tondikiwindi mai nisan kimanin kilomita dari da babban birni Yamai.

Karin bayani: Rundunar tsaron hadin gwiwa a kasashen AES

Tun a karshen watan Yulin 2023 ne, Jamhuriyar Nijar ta koma karkashin jagorancin sojoji da suka karbe mulki domin a cewarsu su dakile tashe-tashen hankulan da 'yan ta'adda ke haddasawa, amma ana ci gaba da kai hare-hare nan da can.