1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan sandan Masar sun fafata da fararen hula

Abdul-raheem Hassan
July 16, 2017

A Masar, jami'an 'yan sanda 31 ne suka ji rauni a fito na fito da mazauna gabar Tsibirin da ke birnin Cairo a yayin rusa gidajen da ba a gina su a kan ka'ida ba.

https://p.dw.com/p/2gdFV
Ägypten Minya Prozess Unterstützer Mohammed Mursi
Hoto: picture-alliance/dpa/K. Elfiqi

Mazauna tsibirin sun yi wa 'yan sandan jifa da duwatsu abin da ya harzika 'yan sandan kai martaninn kariya da hayaki mai sa hawaye. A yanzu dai rahotanni daga cibiyoyin kiwon lafiya na cewar guda daga cikin masu karban jinya ya rasu. Wannan dai na zuwa ne a dai dai lokacin da jami'an tsaron kasar suka tabbatar da kashe wasu mutane tara da ake zargi da ayyukan ta'addanci a yankin Sinai, tare da lalata motoci 15 da ake safarar muggan makamai ta kan iyakar kasar da Libiya.