1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan binda sun hallaka mutane uku a jihar Bayelsa

Salissou Boukari
September 23, 2017

Rundunar 'yan sandan jihar Bayelsa a Najeriya ta sanar da mutuwar mutane uku cikin su har da wani dan sanda guda bayan da masu fashin jirgin ruwa suka yi musu kwanton bauna a yankin Ekebiri na jihar.

https://p.dw.com/p/2ka7A
Nigeria Piraterie
Masu fashin jiragen ruwa a NajeriyaHoto: picture-alliance/dpa

'Yan bindigan dai da ba bayyana ko suwanene ba sun kai wa wani jirgin ruwa mai dauke da jami'an tsaro da kuma fararan hulla hari a yankin Ekebiri a cewar Asinim Butswat mai magana da yawun 'yan sandan jihar Bayelsa, wanda ya ce masu aikin ceto sun iso cikin gaggawa inda suka ceci rayuwar wani dan sanda, da kuma wasu membobin rundunar tsaro ta NSCDC guda hudu, sannan da wasu fararan hulla guda hudu.

Jami'an tsaron da hafaran hullan da ke tare da su, sun fuskanci kwanton bauna ne daga 'yan bindigar kusa da al'ummar Okoron yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa cibiyar mai ta Tebidaba mallakar kampanin Agip Oil na kasar ta Najeriya. Sai dai mazauna yankin sun ce an samu musayar wuta tsakanin jami'an tsaron da 'yan bindigan da ake zaton masu fashin jiragen ruwa ne.