'Yan adawa sun yi nasara a zaben Kuwait
November 27, 2016Talla
Manazarta sun danganta sakamakon zaben da fushin jama'a bisa matakan tsuke bakin aljihu na gwamnati.
Da wannan sakamakon zaben na jiya Asabar dai, zai kasance abu mawuyaci ga gwamnati, ta ci gaba da yin sauye-sayen da take yi da nufin rufe gibin kasafin kudin kasar.
Kamfanin dillancin labaru na gwamnati watau KUNA ta ce, 30 daga cikin wadanda suka lashe kujerun majalisar 50, sabbin mutane ne kuma matasa da mace guda, a zaben da kashi 65 daga cikin 100 na wadanda suka cancanci zabe a Kuwaitin suka kada kuri'unsu.