1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yaƙin Pakistan

March 30, 2007
https://p.dw.com/p/BuOg

A ƙalla mutane 60, su ka rasa rayuka a cikin arangama tsakanin ƙabilu da membobin ƙungiyar Alka´ida a kasar Pakistan a tsukin yan kwanaki 3 da su ka wuce.

Gwamnatin Pakistan na ɗaukar wannan faɗa a matsayin wata nasara,da kuma samun goyan baya daga al´ummar ƙasa , wadda ke sadaukar da rayuwa wajen yaƙar yan taliban.

A shekara ta 2003 dakarun gwamnati Pakistan, sun yi ɓarin wuta da mayaƙan wannan yanki na Waziristan , kamin su rattaba hannu a akan yarjejeniyar zaman lahia, wadda kuma ta tanadi bada haɗin kan ƙabilun a wajen yaƙi da yan taliban.