Wariya, rashin sanin ya kamata, mugunta - tarihin mulkin mallakar Jamus
Mulkin mallakar Jamus a zamanin daular Sarkin Sarakuna, ya gaza cimma burin zama wata daular duniya. Sakamakonsa na da tasiri har yanzu. Wannan shi ne abinda gidan tarihin Jamus ke baje kolinsa a yanzu.
Kayakin tarihi na mulkin mallaka
Bayan da Shugaban Gwamnatin Daular Jamus Otto von Bismarck ya mayar da Namibiya, Kamaru, Togo da wasu yankunan Tanzaniya da Kenya karkashin ikon Jamus, daga 1888 Sarki Wilhelm na 2 ya yi kokarin fadada yankunan da ke karkashin Jamus. Gwamnatin wannan Daula ta nemi "Wuri a Afirka" inji Bernhard von Bülow a 1897 wanda daga baya ya zama Shugaban Gwamnatin Daular.
Yankunan mulkin mallakar Jamus
Bayan ta samu yankin Pasifik (New Guinea ta Arewa, da Bismarck-Archipel, da tsibiran Marshall da Salomon da Samoa) da China tare da hadewa da Daular Ruwanda da Burundi da yankin Gabacin Afirka karkashin Jamus, hakan ya kawo kammaluwar samun yankunan mulkin mallakar a karshen karni na 19..
Tsarin nuna wariya
Farar fata da ke yankunan mulkin mallakar tsiraru ne, amma suna da babbar gata. Ba su fi kashi daya cikin 100 ba. A 1914 Jamusawa kimanin dubu 25 suka zauna a yankunan mulkin mallakar, kasa da rabinsu a Kudu maso Yammacin Afirka. 'Yan asalin yankunan su kimanin miliyan 13 an mayar da su tamkar bayi. An hana su duk hanyoyin samun 'yanci da walwala.
Kisan kare dangi na farko a karni na 20
Kisan kare dangi da aka yi Herero da Nama a yankin da a yau ake kira Namibiya na zama laifi mafi muni a tarihin mulkin mallakar Jamus - a gumurzun da aka yi a Waterberg, akasarin 'yan Herero da suka yi tawaye sun tsere cikin Hamada a 1904. Dakarun Jamus da gangan sun hana su kaiwa ga wuraren da za su samu ruwa. An yi kiyasin cewa 'yan Herero fiye da dubu 60 suka mutu.
Laifin Jamus
'Yan Herero kimanin dubu 16 da suka tsira daga ta'asar, an tsare su a sansanonin gwale-gwale, inda aka ci gaba da yi musu kisa. Har yau ana takaddama game da yawan wadanda aka kashe. Ko wadannan 'yan Herero da suka kanjame sun samu nasarar tserewa? Abinda ke akwai shi ne daukaci sun rasa dukkan abubuwan da suka mallaka na dukiya da na makomar rayuwa.
Sauya tunani a 1907
Sakamakon yakin mulkin malakar ya sa an yi wa hukumar gudanarwar mulkin mallaka a Jamus kwaskwarima, an mayar da hankali a bangarorin kimiyya don amfanin yankunan mulkin mallaka da inganta rayuwar al'ummonin da ke a yankunan mulkin mallakar Jamus. Bernhard Dernburg fitaccen mai kamfani ya dinka wa aikin sake fasalta manufar mulkin mallaka.
Kimiyya da yankunan mulkin mallaka
Baya ga tafiye-tafiye na Dernburg an kuma kafa tare da tallafa wa cibiyoyin kimiyya da fasaha saboda dalilai na mulkin mallaka. Daga ciki an samu kafa wasu bangarorin na jami'o'in Hamburg da Kassel. A 1906 Robert Koch ya jagoranci wata tafiya mai tsawo zuwa gabacin Afirka, don nazarin hanyoyin harbuwa da cutar barci, kamar yadda wannan kundi na magunguna ya nunar.
Daya daga cikin yake-yaken mulkin mallaka mafi muni
A yankin Jamus na gabacin Afirka 'yan asalin yankin su kimanin dubu 100 suka mutu a boren da ake wa lakabi da Maji-Maji a 1905/06. Kungiyoyin al'ummomin yankin sun kulla wani kawancen adawa da mulkin mallakar Jamus. Daga baya ba a yayata batun boren na Maji-Maji a Jamus ba. Ga Tanzaniya boren na zama wani muhimmin lamari na tarihi.
Asarar yankunan mulkin mallaka
Bayan da Jamus ta sha kashi a yakin duniya na daya, an sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya ta Versailles. A lokacin da abinda ta kunsa ya bayyana, an nuna matukar bacin rai a Jamus. Kwalaye kamar wannan sun nuna abinda Jamus ta yi fargabarsa a wancan lokaci: Karfin tattalin arzikinta ya ragu kuma an "sace" mata yankunan mulkin mallaka, barazanar talauci da wahalhalu.
Burin mulkin mallaka a lokacin Nazi
Tunanin mulkin mallaka ya sake kunno kai lokacin 'yan Nazi, ba kawai babban tsarin gwamnatin na shirye-shiryen tsabatacewa da sake tsugunarwa ba. Gwamnatin ta Nazi ta yi ta hankoron sake kwace yankunan mulkin mallakar Jamus, kamar yadda ya fito fili a wannan taswirar da aka lika a wani bangon makaranta a 1938. An so a yi amfani da su a matsayin rumbunan danyun kayayyaki.
Kai komo don yin gyara
An shiga zagaye mai wahala na tattaunawar yadda za a samu bayani bai-daya game da kisan kare dangi da aka yi wa Herero da Nama. Ana samun matsaloli daga bangarorin biyu: Jamus na jan kafa, idan aka tada maganar biyan diyya ta kudi, a Namibiya akwai rashin daidaito na cikin gida. Bada dadewa ba wakilan Herero sun kai karan Jamus a Majalisar Dinkin Duniya game da tattaunawar.