1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Wani farmaki ta sama da Turkiya ta kai ya halaka Kurdawa 34

October 24, 2007
https://p.dw.com/p/C15l
Dakarun kasar Turkiya sun yi lugudan wuta akan wuraren da ake zargi na kungiyar ´yan tawayen Kurdawa na PKK ne dake kan iyakar da Iraqi inda suka halaka mutane 34. Wata majiyar soji ta fadawa kamfanin dillancin labarun Reuters cewa a jiya daddare jiragen saman yakin Turkiya sun kutsa cikin wani yankin Iraqi mai tazarar kilomita 20 daga kann iyakar kasashen biyu. A kuma halin da ake ciki sojojin kasa na Turkiya kimanin 300 na kara dannawa zuwa wannan yanki. A jiya talata FM Turkiya Recep Tayyip Erdogan ya ce ba zai jira har abada ba kafin gwamnatin Iraqi ta dauki wani mataki kan ´yan tawayen wadanda suka halaka dakarun Turkiya 12 a ranar lahadi da ta gabata ba. A kuma halin da ake ciki an ba da umarnin rufe dukkan ofisoshin jam´iyar ma´aikatan Kurdawa dake cikin Turkiya baki daya.