1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Wani soron beni ya ruguje a Kenya

Salissou BoukariApril 30, 2016

Ambaliyar ruwan sama ta haddasa rugujewar wani soron beni a kasar Kenya inda mutane uku suka rasu yayin da wasu da dama suka samu raunuka.

https://p.dw.com/p/1IfhS
Kenia Nairobi Einsturz Wohnhaus
Hoto: picture-alliance/AP Photo/S. A. Azim

A cewar ma'aikatan agaji na Red Cross na kasar ta Kenya kimanin wasu mutane 150 sun samu mafaka a wani kauye da ke yankin da wannan hadari ya faru. Kuma kawo yanzu an samu ceto mutane kusan 60 cikin su har da wani jariri, amma kuma majiyar ta ce akwai mutane da dama karkashin baraguzan ginin. Soron benin dai ya ruguje ne da wajejen karfe tara da rabi na dare agogon kasar a wata unguwa mai cinkoson jama'a ta Huruma da ke arewa maso gabashin birnin Nairobi fadar gwamnatin kasar.