Turkiyya ta gayaci jakadin Jamus a Ankara
September 18, 2017Talla
Wata majiyar diplomasiya ta Turkiyya ta ce jakadin na Jamus Martin Erdmann ya amsa gayatar ce wadda dadewa aka bukaci ya bayyana a ofshin ministan harkokin waje na Turkiyyan. Hukumomin Turkiyyar sun gayaci jakadin ne a game da wata zanga-zangar da magoya bayan kungiyar Kudawa ta PKK ta shirya a Jamus. Wannan dai shi ne karo na 17 da hukumomin Turkiyyar ke gayatar jakadin na Jamus a Ankara.