1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Turkiya ta lashi takobin ganin bayan 'yan tawayen PKK

October 20, 2011

Gamaiyar ƙasa da ƙasa na ci gaba da yin tir da kashe sojojin Turkiya da 'yan tawayen Ƙurdawa suka yi.

https://p.dw.com/p/12vcy
Hoto: picture-alliance/dpa

Babban sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya Ban Ki Moon ya bi sahun ƙungiyar Tarayyar Turai EU da ƙasar Amirka da kuma ƙungiyar ƙawancen tsaro ta NATO wajen yin tir da kisan sojojin Turkiya 24 da 'yan tawayen ƙungiyar Kurdawa ta PKK suka yi. Ya ce ba za a amince da hare haren da Ƙurdawan ke kaiwa ba, inda ya yi kira da girmama 'yancin kan yankunan ƙasashen Iraƙi da Turkiya. Ƙasar Turkiya dai ta ƙaddamar da wani gagarumin farmakin sojojinta a arewacin Iraƙi biyo bayan hare haren da Ƙurdawan suka kai a ranar Laraba, dake zama mafi muni a cikin sama da shekaru uku. An yi imanin cewa an kashe 'yan tawaye 20. Tarayyar Turai da kuma Amirka sun sanya sunan ƙungiyar PKK a jerin sunayen ƙungiyoyin 'yan ta'adda a duniya.

Mawallafi: Mohammad Nasiru Awal
Edita: Umaru Aliyu