Turkiya ta ce ba a yi mata adalci a tattaunawar dsaukar ta cikin EU
December 12, 2006Talla
FM Turkiya Recep Tayyip Erdogan ya yi watsi da shawarar da ministocin harkokin waje na KTT suka yanke ta dakatar da tattaunawar daukar Turkiya cikin kungiyar da cewa ba´a yi adalci ba. Erdogan ya ce kungiyar EU ba zata iya warware rikicin dake tsakanin Turkiya da Cyprus ba saboda haka ya kamata MDD ta tsoma baki. A kuma halin da ake ciki wani jigo na jam´iyar dake jan ragamar mulki a Turkiya, Koksal Toptan ya ce shawarar da EU din ta yanke ba zata sa gwamnati a birnin Ankara ta yi fatali da shirinta na samun wakilci a cikin kungiyar ba. A makon jiya Turkiya ta yi tayin bude tashoshin ta biyu na jiragen ruwa ga yankin Girika na tsibirin Cyprus bisa sharadin cewa za´a dage takunkuma cinikaiya da aka dorawa yankin Turkiya din a Cyprus.