Turkiya na fuskantar matsaloli wajen dakile yaduwar murar tsuntsaye
January 8, 2006Wasu ´yan Turkiya su biyar ciki har da kananan yara maza 2 sun kamu da nau´in H5N1 mai kisa na cutar murar tsuntsaye a daidai lokacin da kwayoyin cutar ke ci-gaba da bazuwa a yammacin kasar zuwa nahiyar Turai. A halin da ake ciki hukumomin Turkiya na fuskantar matsaloli ta yadda zasu dakile yaduwar kwayoyin cutar. A halin da ake ciki wata tawagar kungiyar lafiya ta duniya WHO ta tashi zuwa yankunan da cutar suka bulla a gabashin Turkiya, don kimanta irin martanin da gwamnati ta mayar tare da duba yiwuwar ko kwayoyin zasu iya bazuwa tsakanin ´yan Adam. Wani jami´in ma´aikatar kiwon lafiya ya fadawa kamfanin dillancin labarun kasar cewa mutane biyu a birnin Van dake gabashin kasar da kuma sauran 3 a birnin Ankara sun kamu da kwayoyin nau´in H5N1. Yanzu haka dai yawan wadanda suka kamu da kwayoyin cutar mai kisa sun kai mutum 9 dukkansu yara kanana, in banda mutum daya.