1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Turkiya: Gyara ga kundin tsarin mulki

Lateefa Mustapha Ja'afar
March 27, 2017

Daga wannan Litinin har zuwa ranar tara ga watan Afrilu mai zuwa, 'yan kasar Turkiyya da ke zaune a kasashen ketare za su fara kada tasu kuri'a a kan kwaskware kundin tsarin mulkin kasarsu.

https://p.dw.com/p/2a3vJ
Kuri'ar yin gyara ga kundin tsarin mulkin Turkiya
Kuri'ar yin gyara ga kundin tsarin mulkin TurkiyaHoto: picture-alliance/AA/H. M. Sahin

In har sakamakon kuri'ar raba gardamar ya amince da yi wa kundin tsarin mulkin Turkiyan kwaskwarima, hakan zai ba wa Shugaba Recep Tayyip Erdogan damar fadada ikonsa. A nan Jamus 'yan kasar ta Turkiyya su kimanin sama da miliyan guda da suka cancanci kada kuri'a, za su sauke wannan nauyi a kananan ofisoshin jakadancin kasar da ke fadin Jamus. A can Turkiyya a ranar 16 ga watan Afrilu za a kada kuri'ar raba gardamar a kan kwaskware kundin tsarin mulkin. Wata takaddama a kan gangamin yakin neman zabe da 'yan siyasar Turkiyya a Jamus suka so yi, ta janyo tsamin dangantaka tsakanin kasashen biyu lamarin da ya sa Shugaba Erdogan ya soki Jamus da bin manufofin 'yan Nazi, kalaman kuma da 'yan siyasa a Jamus din da ma nahiyar Turai suka yi tir da su.