1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tunawa da kulla zumuntar Jamus da Faransa

September 22, 2012

Daga Abokan gaba zuwa abokan arziki, Jamus da Faransa sun yi waiwaye akan ranar da suka sasanta da juna bayan yakin duniya na biyu.

https://p.dw.com/p/16Cq2
German Chancellor Angela Merkel and French President Francois Hollande arrive at the Baroque palace of Ludwigsburg, southwest Germany, on September 22, 2012 for a ceremony to mark a watershed 1962 speech by Charles de Gaulle, then President of France, to German youth in Ludwigsburg. AFP PHOTO / THOMAS KIENZLE (Photo credit should read THOMAS KIENZLE/AFP/GettyImages)
Hoto: THOMAS KIENZLE/AFP/GettyImages

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel da takwaranta na Faransa Francois Holland sun gudanar da bikin tunawa da ranar da kasashen biyu sasanta da juna bayan yakin duniya na biyu. Shugaban Faransa Francois Holland ya yi tattaki zuwa birnin Ludwigsburg dake kudu maso gabashin Jamus domin haduwa da shugabar gwamnati Angela Merkel wajen gudanar da bikin zagayowar ranar ta sake kulla zumuntar kasashen biyu. A wannan wuri ne shekaru 50 da suka wuce tsohon shugaban Faransa Charles de Gaulle ya gabatar da jawabi ga matasa Jamusawa. An yabawa jawanin na Charles de Gaul a matsayin babban mataki na karfafa zumunta tsakanin Jamus da Faransa bayan da kasashen biyu suka gwabza fada a yakin duniya inda ma ake danganta su a matsayin manyan abokan gabar juna. Tsohon shugaban Faransar Charles de Gaul da takwaransa na Jamus na wancan lokaci Konrad Adenauer sune suka dabbaka yunkurin sasantawar kasashen biyu. Wannan yunkuri na kasashen biyu ne ya zama tambarin hadin kan nahiyar turai baki daya.

Mawallafi: Abdullahi Tanko Bala
Edita: Yahouza Sadissou Madobi