Trump: 'Yan jarida ba su da gaskiya
January 23, 2017Sama da mutane miliyan biyu ne dai suka yi tururuwa zuwa biranen Amirka, a dai-dai lokacin da mata ke gudanar da gangamin adawa da kaskanci da Trump ya yi musu.
Fitattun mata a fannoni daban-daban da masu fafutukar 'yanci ne dai suka yi dafifi a birnin Washington, a daidai lokacin da Trump ya zargi kafofin yada labarai kan abin da ya kira rashin gabatar da rahotannin gaskiya game da yawan wadanda suka halarci bikin rantsar da shi a ranar Jumma'ar da ta gabata ba. Sabon shugaban na Amirka bai ce uffan game da wannan gangamin adawa ba, wanda ke zuwa a ranarsa ta farko akan madafan iko.
Duk da cewar babu cikakkun alkaluman wadanda suka shiga wannan zanga-zangar lumana, wadanda suka shirya sun ce sama da mata miliyan guda ne suka hallara a birnin washinton kadai, daura da wasu kimanin 600 da ake gudanarwa a sassa daban-daban na duniya. Matan wadanda suka hada da 'yan makaranta sun jaddada cewar wajibi ne a daraja 'yancin mata.