1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Trump: 'Yan jarida ba su da gaskiya

Zainab Mohammed Abubakar
January 23, 2017

Shugaban Amirka Donald Trump ya ce kafofin yada labarai ba su fadi gaskiya dangane da yawan mutanen da suka halarci bikin rantsar da shi a ranar Jumma'a ba.

https://p.dw.com/p/2WDVP
USA Amtsübernahme Trump
Hoto: Reuters/C. Barria

Sama da mutane miliyan biyu ne dai suka yi tururuwa zuwa biranen Amirka, a dai-dai lokacin da mata ke gudanar da gangamin adawa da kaskanci da Trump ya yi musu.

Fitattun mata a fannoni daban-daban da masu fafutukar 'yanci ne dai suka yi dafifi a birnin Washington, a daidai lokacin da Trump ya zargi kafofin yada labarai kan abin da ya kira rashin gabatar da rahotannin gaskiya game da yawan wadanda suka halarci bikin rantsar da shi a ranar Jumma'ar da ta gabata ba. Sabon shugaban na Amirka bai ce uffan game da wannan gangamin adawa ba, wanda ke zuwa  a ranarsa ta farko akan madafan iko.

Duk da cewar babu cikakkun alkaluman wadanda suka shiga wannan zanga-zangar lumana,  wadanda suka shirya sun ce sama da mata miliyan guda ne suka hallara a birnin washinton kadai, daura da wasu kimanin 600 da ake gudanarwa a sassa daban-daban na duniya. Matan wadanda suka hada da 'yan makaranta sun jaddada cewar wajibi ne a daraja 'yancin mata.