1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tawagar kungiyar taraya Afrika ta kasa cimma burin nada saban Praminista a kasar Kote Divoire

November 23, 2005
https://p.dw.com/p/BvJr

Shugaban kungiyar Gammaya Afrika, Olesegun Obasanjo, da na kungiyar ECOWAS, Tanja Mamadu, da kuma shugaban Afrika ta kudu Tabon Mbeki, da ke shiga tsakani a rikicin Kote Divoire, da su ka kai ziyara jiya a wannan kasa, sun kasa cimma burin su, na zaben saban Praminista.

Tawagar shuwagabanin, ta tantana da gwamnatin kasar Kote Divoire, da yan adawa, da kuma yan tawaye, a game da wannan batu mai sarkakiya.

Bayan tankade da reraye sun cimma daidaito na samun yan takara 2, daga jerin jimilar mutane 16 da a ka gabatar da sunayen su , wanda daga cikin su ya cencenta a tsamo saban Praministan, da bangarori baki daya za su yi masa mubai´a.

Saidai a cewar shugaban Obasanjo, daga wannan yan takara 2 ,babu wanda ya cika sharrudan da za su gamsar da kowa.

A game da haka tawagar shuwahabanin kasashen zata sake komawa nan da kwanaki 10 masu zuwa, domin ci gaba da tantanawa.

Idan za a iya tunawa ,a satin da ya wuce, yan tawaye , sun yi watsi da jerin sunayen 16, da a ka gabatar masu, dalili da babu sunan shugaban su Guillaume Soro a ciki.