1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tattauna batun aikin hajji tsakanin Iran da Saudiyya

Salissou BoukariApril 15, 2016

A wani mataki na shirin fuskantar ayyukan hajjin bana, hukumomin Saudiyya da na Iran sun soma wata ganawa a birnin Makka.

https://p.dw.com/p/1IWbU
Saudi-Arabien hunderte Tote bei Massenpanik in Mekka
Mahajjata a birnin Makka na kasar SaudiyyaHoto: Reuters/A. Masood

Wannan dai ita ce haduwa ta farko a hakumance tsakanin hukumomin biyu na Saudiyya da Iran tun bayan tsinke huldar diflomasiyyar da suka yi a watan Janairu da ya gabata, bayan da wasu masu adawa da kisan da aka yi wa shehin malamin nan na Shi'a a Saudiya, suka kai hari a ofishin jakadancin kasar ta Saudiyya a birnin Teheran.

A baya dai Saudiyya ta haramta dukannin wata zirga-zirgan jiragen sama tsakaninta da Iran sakamakon katse huldar diflomasiyyar. Kasashen biyu dai na da mabanbantan ra'ayoyi bisa fannoni da dama, kamar na yaki a kasar Siriya, inda Iran ke tallafawa gwamnatin Bashar Al-Assad yayin da Saudiyya ke taimaka wa 'yan tawaye.