1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tattalin arzikin Najeriya na farfadowa

Abdul-raheem Hassan
February 28, 2017

Sabbin alkaluman da ta wallafa a wannan Talatar sun bayyana cewa kasar ta samu bunkasar arziki, bayan koma baya na kashi daya da digo biyar cikin dari da ta samu a bara.

https://p.dw.com/p/2YNg1
Nigeria Symbolbild Korruption
Hoto: picture-alliance/AP Photo/S. Alamba

Hukumar kididdigar tattalin arziki ta kasa, ta ce faduwar tattalin arzikin Najeriya na da alaka da faduwar farashin man a kasuwannin duniya da kuma yadda tsageru a kudancin kasar ke fasa bututan mai, da kuma faduwar darajar takardar kudi ta Naira.

Najeriya dai na dogaro ne kacokan a kan arzikin man fetur da Allah ya hore mata, wajen samun kudin shiga. Sai dai kuma gwamnatin Muhammadu Buhari, ta fitar da sabon tsari na fito domin shigar da karin kudi aljuhunta. Wannan ya sa masana ke hasashen komadar tattalin arzikin kasar abana da daidatuwar farashin danyen mai a kasauwannin duniya.