1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tashin hankali a Thailand

May 19, 2010

Sojoji suna buɗe wuta kan masu zanga zanga a Thailand, a wani yunƙurin kawar da masu neman kifar da gwamnati

https://p.dw.com/p/NRW5
Sojin Thailand a fagen dagaHoto: AP

Tankokin sojin gwamnatin Thailand sun fara ragargaza shingayen da masu adawa da gwamnati da ke bore suka kafa a cibiyar kasuwancin ƙasar dake Bangkock. Gwamnatin ƙasar ta ƙira masu zanga zangar da su yi sorenda nan take. Dubban masu boren waɗanda aka sani da masu jajayen riguna, har yanzu ke fake a sansanonin da suka kame a cikin babban birnin ƙasar. Kakakin gwamnatin ƙasar ya bayana cewa, " Domin mu samu kawo ƙarshen tashin hanklin da ya ɓarke a 'yan kwanakinnan mun keɓe wassu wurare, waɗande dole a samar da tsaro, kuma za mu samar da tsaro ga al'umma." Wannan matakin basani ba sabo da soji suka fara ya zo ne bayan da tattaunawa tsakanin gwamnati da masu boren ta bi ruwa, yanzu dai kwana biyar kenan ana arangama tsakanin sojoji da masu neman a sauke gwamnati, abinda ya hallaka mutane kimanin 40.

Mawallafi: Usman Shehu Usman

Edita: Mohammed Nasiru Awal