1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tashe tashen hankula Kongo gabanin zaben gama gari a ranar lahadi

July 25, 2006
https://p.dw.com/p/BupD
Kwanaki biyar gabanin zabukan shugaban kasa da na ´yan majalisar dokoki da za´a gudanar a kasar JDK, an yi mummunar arangama tsakanin dubban magoya bayan ´yan adawa da ´yan sanda a birnin Kinshasa. ´Yan adawan sun ta jifar ´yan sanda da duwatsu da bama-baman kwalaba kana kuma sun yi kira da a dage ranar kada kuri´ar. Su kuma a nasu bangare ´yan sanda sun yi amfani da hayaki mai sa hawaye da kulake akan gungun masu zanga-zangar. Don ba da kariya a lokacin zaben rundunar sojin Jamus ta Bundeswehr ta tura sojoji kusan 800 zuwa Kinshasa.