Taron tattalin arzikin duniya a birnin Davos
January 26, 2006Talla
A yau aka shiga rana ta biyau na taron tattalin arzikin kasashe na duniya dake gudana a birnin Davos na kasar Swistzerland. Taron wanda ya sami halartar shugabanni da masana tattalin arziki, siyasa da kuma kasuwanci ya yi tsokaci a game da bunkasar tattalin arziki na nahiyar Asia. Batun tattalin arzikin kasashen China da India shi ne yafi daukar hankali a zauren taron.Shugabannin kimanin 2,300 daga kasashe daban daban na duniya ke halartar taron wanda zaá shafe tsawon kwanaki biyar ana gudanar da shi. A jawabin ta yayin bude taron shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta baiyana matakan tada komadar tattalin arziki da sabuwar gwamnatin ta ke da nufin aiwatarwa.