Taron shugabanin EU a Bruxelles
March 9, 2007Talla
An shiga kwana na 2, a taron shugabanin ƙasashen ƙungiyar gamayya turai da aka fara jiya, a birnin Bruxelles na ƙasar Belgium.
Babban batun da ake ajendar taron a yinin yau,ya jiɓancin ɓullo da sabin hanyoyin mallakar makamashi don yaƙi da ɗumamar yanayi.
Shugabar gwamnatin Jamus da ahayin yanzu ke jagorantar EU ta bayyana sabanin ra´ayoyi da su ka sa tarnaki ga wannan batu a mahaurorin da su ka gudana jiya, saidai a cewar ta, akwai alamun cimma daidaito a kan batun.
A ɗaya hannun shugabanin sun tantana, a kann jaddawwalin bikin cikwan shekaru 50 da girka ƙungiyar taraya turai.
A nan ma, an fuskanci saɓanin ra´ayoyi a game da batun faɗaɗa wannan ƙungiya, da kuma hanyoyin cuɗe ni in-cuɗe ka, tsakanin ƙasashe 27 membobin ta.