Taron limaman Katolika a Jamus.
September 20, 2010Talla
Bisa matsin lambar da suka fuskanta, shugabannin cocin Katolika guda 27 a nan Jamus sun fara taron yini hudu a birnin Fulda na yankin tsakiyar kasar nan, domin tattaunna biyan diyya ga yaran da limaman cocin suka yi lalata da su a wani lokaci can baya. Limaman sun ce ba su tatance kudaden da za su bayar a matsayin diyyar ba. Wadanda wannan tabargazar ta shafa a mujami'ar garin Jesuit dai sun bukaci a ba kowannensu diyyar euro dubu 82, amma sai limaman suka ce sun daidaita kan ba da kashi daya daga cikin goma na wannan kudi. A farkon wannan shekarar ne dai aka fallasa tabargazar yin lalata da kananan yara da ta auku a cocin Katolika daga shekarun 1950 zuwa 1980.
Mawallafiya: Halima Balaraba Abbas
Edita: Zainab Muhammad Abubakar