1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taron Kungiyar AU

March 10, 2006
https://p.dw.com/p/Bv5P

Shugaban hukumar kungiyar taraiyar Afrika ya baiyana rashin jin dadinda dangane da halin da yan gudun hijira na Darfur suke ciki.

Alpha Umar Konare ya fadi haka ne a lokacin ziyararsa zuwa birnin Berlin.

A yau ne dai ake sa ran kungiyar Taraiyar Afrika AU zata yi taronta a birnin addis Ababa na kasar Tanzania domin yanke shawara akan ko ta bukaci Majalisar Dinkin Duniya karbar ragamar aiyukan wanzar da zaman lafiya a Darfur.

Amurka da Kungiyar Taraiyar Turai dai suna ci gaba da matsawa kasar Sudan lamba data amince da kasancewar dakarun Majalisar Dinkin Duniya a Darfur,inda yan tawaye da kungiyoyi masu dauke da makamai suke ci gaba da kashe kashen rayuka a yankin.