1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taron kasashen tarayyar Turai da na bakin tekun Bahar Rum

November 27, 2005
https://p.dw.com/p/BvJE

Jim kadan gabanin a fara taron kolin kasashen kungiyar tarayyar Turai da takwarorinsu na yankin tekun Bahar Rum, MDD ta yi kira da a kara ba da kariya ga ´yan gudun hijira daga Afirka. Wata mai magana da yawun hukumar taimakawa ´yan gudun hijira ta MDD ta yi zargin cewa sau da yawa ana daukar ´yan gudun hijirar tamkar bakin haure. Muhimman batutuwan da za su dauki hankali a taron kolin na yini biyu da za´a fara yau lahadi a birnin Barcelona na kasar Spain sun hada da na ´yan gudun hijira da yaki da ´yan ta´adda da kuma shirye shiryen kirkiro wani yankin ciniki maras shinge. Sabuwar shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel na daga cikin shugabannin tarayyar Turai da zasu halarci taron kolin.