1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taron AU karo na 30 ya cimma matsaya kan wasu batutuwa

Gazali Abdou Tasawa
February 1, 2018

Taron koli na Kungiyar Tarayyar Afirka karo na 30 da ya gudana a birnin Adis Ababa ya tattauna batutuwa da dama na bunkasa tattalin arzikin nahiyar da kuma wasu matsaloli da ke ci wa nahiyar tuwo a kwarya.

https://p.dw.com/p/2ruPk
Äthiopien Addis Abeba Afrikanische Union Gipfel
Hoto: picture-alliance/AA/M. W. Hailu

Taron koli na Kungiyar Tarayyar Afirka ta AU karo na 30 da ya gudana a birnin Addis Ababa na kasar Habasha ya mayar da hankali kan batutuwa da ke ci wa nahiyar tuwo a kwarya a halin yanzu da suka hada da matsalar karancin kudin gudanarwar kungiyar, da ta 'yan gudun hijira da kuma ta yake-yake da rigingimun siyasar da ake fama da su a wasu kasashen nahiyar. Kazalika taron ya duba batun yaki da cin hanci da rashawa a nahiyar kana ya amince da wasu matakai kan inganta sufurin jiragen sama a nahiyar da dai sauran batutuwa.