Takun saƙar Uganda da 'yan janjawid
June 15, 2010Talla
Ƙasar Uganda ta zargi sojojin sa kai na Sudan da murƙushe mata sojoji ba tare da wani ƙwaƙwaran dalili ba. Cikin wata hira da yayi da jaridar New Vision a birnin kampala, hapsan hapsoshin sojojin Uganda, wato janar Aronda Nyakairima ya ce 'yan janjawid sun kashe sojojinsu 10 a jamhuriyar Afirka ta tsakiya.
Ƙungiyar 'yan tawaye ta LRA ce gwamantin Uganda ta fara zargi da wannan aika-aika kafin daga bisani ta ƙaryarta labarin. Dama dakarun na Uganda na far ma 'yan awaren na LRA ne a maɓuyarsu da ke jamhuriyar Afirka ta tsakiya.
Mawallafi: Mouhamadou Awal
Edita: umaru Aliyu