Taba Ka Lashe: 27.09.2017
September 29, 2017Talla
A ci gaba da kokarin bunkasa harshen Hausa da al'adun Hausa a makonni baya sashen harsuna da al'adun Afirka na jami'ar Ahamadu Bello da ke Zaria a jihar Kadunar Arewacin Najeriya ya shirya wani taron kwanaki biyu na masana tarihi da harsunan Afirka inda aka mayar hankali tare da jaddada muhimmancin harsunan asali da ma yadda za a samo ma'anoni na wasu kebabbun kalmomi na kimiyya da fasaha.