Taba Ka Lashe: 08.02.2017
February 10, 2017Talla
Malaman addinai da kungiyoyin farar hula da ke fafutukar tabbatar da zaman lafiya a Najeriya na ci gaba da shirya wasannin motsa jiki tsakanin matasa Musulmi da Kirista da masu bin addinan gargajiya a wani mataki na karfafa zamantakewa tsakanin al'umma. A Kaduna da ka arewacin Najeriya an shirya irin wannan wasan motsa jiki don kara fahimtar juna tsakanin al'ummar wannan jiha da ta yi suna wajen fama da tashe tashen hankula masu nasaba da addini.