1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojojin Libya sun fatattaki IS daga tsakiyar birnin Sirte

Mohammad Nasiru AwalAugust 11, 2016

Rundunar sojin Libya ta ce IS ta yi mummunan rauni ta yadda ba za ta iya tinkarar sojojin kasar ba musamman a birnin Sirte.

https://p.dw.com/p/1Jgns
Libyen Sirte Kampf gegen IS
Hoto: picture alliance/ZUMA Press/H. Turkia

Kakakin sojojin Libya da ke fafatawa a birnin Sirte Kanal Mohammed al-Ghasri ya ce kungiyar IS ba ta da karfin dakarun da za su iya turje wa dakarun Libya a Sirte bayan da sojojin Libya suka sake kwace iko da cibiyar babban taro da ke tsakiyar birnin, inda 'yan tarzoma suka taba kafa bakar tutarsu ta Jihadi. Kanal Mohammed al-Ghasri ya ce yanzu an gama da mayakan na IS a wannan birni.

Ya ce: "A iya saninmu dai an yi gumurzu na karshe bayan mun karbi iko da cibiyar taro ta Ouagadougou kuma a garemu IS ta kare. Za su iya kokarin tserewa ko kashe kansu, amma ba su da karfin da za su iya fuskantar dakarunmu. Ga ra'ayin soja, IS ta kau bayan mun karbi iko da cibiyar ta Ouagadougou."

A wannan Alhamis dai dakarun Libya sun mamaye yankunan da suka kwace daga IS suna kuma tono nakiyoyin karkashin kasa a kewayen cibiyar taron da ke a birnin na Sirte.