Sojan ISAF ɗaya ya rasa rai a Afghanistan
August 3, 2006Talla
Dakarun Taliban na kudanci Afghanistan ,sun kashe ƙarin soja ɗaya na rundunar ƙasa da ƙasa ta ISAF, a sahiyar yau almahis.
Sojan ya rasa ran sa sanadiyar, tarwasewar wata Bom, a kussa da Khandar.
Wannan shine soja na 4 da ya mutu a ƙasar, tun bayan da ƙungiyar tsaro ta NATO, ta ɗauki jagorancin ayyukan sojojin ƙasa da ƙasa a Afgahanistan, ranar litinin da ta wuce.
An ɓangaren yan taliban, rundunar ISAF ta bayyana kashe mayaƙa a kalla 10 tsakanin jiya zuwa yau.