1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Slovenia ta ƙarbi jagorancin Ƙungiyyar Eu

Ibrahim SaniJanuary 1, 2008
https://p.dw.com/p/Cifb

Ƙasar Slovenia ta ƙarbi jagorancin Ƙungiyyar Tarayyar Turai Eu, a safiyar yau talata. Batun makomar yankin Kosovo da kuma kundin tsarin mulƙin ƙungiyyar, abubuwa ne da za su kasance ja- gaba, a lokacin wannan jagoranci. Slovenia ta ƙarbi jagorancin ne na tsawon watanni shida daga ƙasar Portugal. Ana sa ran Slovenia za ta miƙa ragamar ƙungiyyar ga Faransa, a ranar ɗaya ga watan yulin wannan shekara. A waje ɗaya kuma ƙasashen Cyprus da Malta, sun shiga cikin da´irar ƙasashe dake amfani da kuɗin Yuro.