1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Siriya ta tsira daga takunkumi

Abdul-raheem Hassan
February 28, 2017

Kasashen Rasha da China sun yi amfani da karfin iko na kin amincrewa da kudirin kwamitin sulhu na Majasalisar Dinkin Duniya da ke son ladabtar da wasu jami'an gwamnati Siriya.

https://p.dw.com/p/2YPgG

Daman dai kasashen Birtaniya da Faransa da kasar Amirka ne ke kan gaba wajen ganin hakar su ta cimma kuri'ar sanya wa gwamnatin Siriya takunkumin, bisa zargin ta da amfanin da makamai masu guba a yakin da ta ke yi da 'yan 'yan tawaye.

Kwamitin na Majalisar Dinkin Duniya na bukatar kuri'u na akalla kashi tara da ke goyon bayan kudirin, kan a  amince da zartas da ko wani mataki. Wannan dai shi ne karo na bakwai da kasar Rasha ke amfani da karfin ikonta na marawa Siriya baya, sai kuma a wannan karon da ta samu hadewar kasar China.

Ana dai dab da sanya sunayen wasu kwamandojin Siriya 11, dama kasar baki daya cikin jerin kasahen da ke amfani da makamai masu guba, amma dai gwamnatin Bashar al-Assad ta sha musanta wannan zargi.