1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Siriya: Gwamnati ta kwaci Deir Ezzor daga IS

Salissou Boukari
November 3, 2017

Sojojin gwamnatin Siriya masu samun goyon bayan Rasha sun kwace birnin Deir Ezzor daga hannun mayakan IS a cewar kungiyar da ke sa ido kan kare hakin bil-Adama ta (OSDH) a kasar ta Siriya.

https://p.dw.com/p/2mxDI
Syrien Krieg - Kämpfe in Deir ez-Zor
Hoto: Getty Images/AFP

Tun dai a jiya kafofin yada labaran gwamnatin ta Siriya suka sanar cewa akwai babban ci gaba da dakarun gwamnatin ke samu a birnin na Deir Ezzor yanki mai arzikin man fetur da ke gabashin kasar iyaka da Iraki. Sai dai kuma a hakumance gwamnatin ta Siriya ba ta ayyana kwace birnin ba. Hakan dai na kara tabbatar da irin mawuyacin halin da 'yan kungiyar ta IS ke ciki a halin yanzu, inda take ci gaba da fuskantar babban koma baya. 

Kungiyar kare hakin bil-Adama ta kasar ta Siriya mai cibiya a birnin London na Britaniya ta OSDH, ta ce an dakatar da harbe-habe, kuma tuni aka soma ayyukan tone nakiyoyi da 'yan jihadin suka bizne a wurare daban-daban. Sai dai kuma wata majiya ta sojan kasar ta Siriya ta ce sun dai kwace sama da kashi 80 ne na birnin.