Siri Lanka ta nemi taimako
May 28, 2017Talla
Masu aikin ceto a kasar Siri Lanka sun gano karin mutanen da suka hallaka sakamakon zabtarewar kasa da aka samu bayan kwashe kwanaki biyu ana sheka ruwan sama. Gwamnati ta tabbatar da mutuwar fiye da mutane 150 yayin da wasu fiye da 110 suka bace kuma ake ci gaba da nama.
Gwamnatin kasar ta Siri Lanka ta bukaci taimakon kasashen duniya, saboda barazanar da kimanin mutane 100,000 suke fuskanta wadanda bala'in ya shafa. Tuni wasu kasashe suka fara kai dauki.