1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Shugabar tawagar dakarun EU ta fice daga Nijar

March 18, 2024

Shugabar kawancen dakarun EU da ke aikin wanzar da zaman lafiya a Sahel Katja Dominik, ta shaki iskar 'yanci bayan sojojin Nijar sun hana ta ficewa daga kasar, acewar kamfanin dillancin labaran Jamus.

https://p.dw.com/p/4drkr
Sojojin EUCAP dake aikin wanzar da zaman lafiya a Sahel a wani taro a Nijar.
Sojojin EUCAP dake aikin wanzar da zaman lafiya a Sahel a wani taro a Nijar.Hoto: Marou Madougou Issa/DW

Shugabar kungiyar dakarun Katja Dominik 'yar kasar Jamus da shugaban kwamitin tsare-tsaren dakarun Mads Beyer 'dan kasar Denmark sun sauka a birnin Brussels a yammacin jiya lahadi 17 ga watan Maris 2024.

Karin bayani:An bukaci wasu dakaru su fice daga Jamhuriyar Nijar 

Mai magana da yawun EU ta shaidawa manema labarai cewa tuni dukkan dakarun dake aikin wanzar da zaman lafiya a Jamhuriyar Nijar suka fice daga yankin na yammacin Afrika.

Karin bayani:  Sahel: Kafa rundunar sintiri ta Turai

Kimanin sojojin kawancen dakarun EU 120 ne ke aiki a Jamhuriyar Nijar wajen horas da sojojin kasar a wani yunkuri na yaki da 'yan ta'adda da 'yan bindiga harma da masu hada-hadar miyagun kwayoyi zuwa ga dakile ayyukan masu safara da mutane.