Shugabar Mauritius za ta ajiye aiki
March 9, 2018Talla
Shugabar kasar Mauritius Ameenah Gurib-Fakim za ta sauka daga mukaminta, bayan zarginta da aka yi da wata badakalar da ta shafi kudade. Shugaba Ameenah Grib-Fakim wacce Farfesa ce, ita ce kadai shugaba mace a nahiyar Afirka a yanzu. Tana fuskantar zargi ne na amfani da wani katin cirar kudi na wata kungiya, inda ta ke biyan bukatunta da su.
A cewar firaministan kasar Pravind Jugnauth, shugabar kasar za ta sauka ne bayan bikin cikar kasar shekaru 50 da samun 'yanci wanda za a yi a ranar Litinin na makon gobe.