1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaban sojoji ya gargadi jam'iyyar Mugabe

Yusuf Bala Nayaya
November 13, 2017

Kore-koren da ake yi wanda ke da buri na kakkabe wasu kusosi a jam'iyyar ta masu mulki ya zama dole a tsayar da shi take a cewar Janar Constantino Chiwenga.

https://p.dw.com/p/2nYKf
Simbabwe Robert Mugabe mit Ehefrau Grace in Harare
Hoto: Reuters/P. Bulawayo

Shugaban rundinar sojan kasar Zimbabuwe a wannan rana ta Litinin ya bukaci a dakatar da kore-kore da ake a jam'iyyar ZANU-PF, abin da ke zuwa bayan korar mataimakin shugaban kasa Emmerson Mnangangwa, ya kuma yi gargadin cewa soja na iya kawo dauki a rudanin da kasar ke neman fadawa.

Kore-koren da ake yi wanda ke da buri na kakkabe wasu kusosi a jam'iyyar ta masu mulki ya zama dole a tsayar da shi take a cewar Janar Constantino Chiwenga a lokacin da yake jawabi a taron manema labarai wanda kimanin manyan sojoji a kasar 90 suka halarta a hedikwatar sojan kasar ta Zimbabuwe.

A cewarsa wadanda ke neman haifar da rudani a kasar su kuka da kansu, idan har suka nemi dagula lamura ya zama dole soja su sa hannu don gudun kada a wargaza kasar.