Shugaban Jamus Köhler ya kalubalanci manufar EU game da Afirka
January 13, 2007A ziyarar da yake ci-gaba da kaiwa kasar Ghana shugaban tarayyar Jamus Horst Köhler yayi kira da a samar da abin da ya kira dangantaka ta hakika tsakanin nahiyoyin Turai da Afirka. A lokacin da yake jawabi a gaban wani taro karo na biyu na wani zauren tattaunawa da Afirka da ya kirkiro, shugaba Köhler ya ce sassan biyu ka iya yin koyi da juna a batutuwa da dama. A yau aka bude taron na yini biyu a birnin Accra na kasar Ghana. A lokaci daya kuma shugaban ya yi suka ga manufofin tattalin arzikin KTT game da Afirka. Ya ce kungiyar EU ba zata a iya a hannu daya tana kafa shingen ciniki sannan a daya hannun tana cike kasuwannin Afirka da kayakin ta musamman na abinci. Ya ce hakan na kawowa Afirka cikas a kokarin ta na samarwa kanta kayan abinci da take bukata. Köhler ya yi kira ga kasashen Afirka da su girmama hakkin dan Adam.