1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sabbin gwamnoni a Sudan ta Kudu

Yusuf BalaDecember 30, 2015

Shugaba Kiir na Sudan ta Kudu ya ce dole ne sabbin gwamnonin su yi aiki da yarjejeniyar zaman lafiya da 'yan adawa.

https://p.dw.com/p/1HVwF
Südsudan Präsident Salva Kiir
Shugaba Salva KiiHoto: picture-alliance/dpa/P. Dhil

Shugaban kasar Sudan ta Kudu Salva Kiir ya bukaci sabbin gwamnonin da aka nada a kasar su tabbatar da aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiya da aka yi tsakanin gwamnatinsa da bangaren 'yan adawa a karshen watan Agusta.

Da yake jawabi a lokacin rantsar da sabbin gwamnonin a ranar Talata shugab Kiir ya bayyana cewa ba zai lamunci duk wani yunkuri na cin hanci da rashawa ba, abin da ya bayyana da zama cutar daji a kasar .

"Muna bukatar gwamnati mai inganci, haka kuwa abu ne da zai samu ta hanyar shugabanci nagari, wanda babu batun cin hanci da rashawa a cikinsa, abinda ke zame mana tamkar cutar daji wacce zamu tashi tsaye baki daya mu yi yaki da ita".

A ranar 24 ga watannan na Disamba ne dai shugaba Kiir ya rushe jihohi 10 na Sudan ta Kudu da samar da sabbin jihohi 28 a yunkurin da ke shan suka ta 'yan adawa.