1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaba Karzai ya zargi NATO da rashin ba gwamnatinsa hadin kai

June 23, 2007
https://p.dw.com/p/BuI1

Shugaban Afghanistan Hamid Karzai ya yi suka da kakkausan lafazi akan dakarun kungiyar tsaro ta NATO a dangane da yawan asarar fararen hula a hare haren da kungiyar ke kaiwa a Afghanistan. Karzai ya fadawa manema labarai cewa rayukan ´yan Afghanistan na da daraja kamar na sauran al´umomi. Karzai ya ce dakarun NATO ba sa neman shawarar gwamnatinsa a aikace aikacensu. Shugaban na Afghanistan ya ce idan aka ci-gaba a haka to ko shaka babu yakin da ake yi da ´yan ta´adda na cikin hadari.

O-Ton Karzai:

“Amfani da karfi fiye da kima da rashin tuntubar gwamnatin Afghanistan ke janyo asarar rayukan. Dole ne su karfafa rundunar soji da ta ´yan sandan Afghanistan tun daga toshen ta. Kamata yayi sun san cewa Afghanistan kasa ce ta dabam mai kuma al´adu dabam. Saboda haka tun daga yanzu ya zama dole su yi aiki kamar yadda mu muke bukatar su yi a nan.”

Wannan sukan ya zo ne sakamakon mutuwar fararen hula kimanin 90 sakamakon hare hare da sojojin NATO ke kaiwa a fadin kasar ta Afghanistan a cikin mako guda kacal. A kuma halin da ake ciki an halaka ´yan tawayen Taliban kimanin 60 a jerin hare hare ta sama da kuma ta kasa da dakarun kawance karkashin jagorancin NATO suka kai a lardin Paktika da ke gabashin Afghanistan.