Cikin shirin za a ji yadda wata gamayyar kungiyoyin siyasa a Nijar ta fito ta mara wa gwamnatin shugaba Mouhamadou Issoufou baya kan tsarin kasafin kudin kasar da kuma wasu manufoyin gwamnatin da yake ja. Hakan kuwa sun yi shi ne duk da rashin turkiyar da talakawa da wasu kungiyoyn fararen hula suka yi kan tsarin tafiyar gwamnatin da suka ce mai tsada ce ga masu karamin karfi.