Cikin shirin za a ji cewa a Jamhuriyar Nijar hadin gwiwar kungiyoyin farar hula masu adawa da dokar kasafin kudi ta bana da gungun kawancen jam’iyyun adawa sun mayar da martani ga jam’iyyun da ke mulki, bayan wata sanarwar da ta fito mai zargin 'yan adawar kasar da neman tayar da husuma. A Najeriya hukumomin kasar sun dauki matakan kawo karshen rikicin manoma da makiyaya.