A cikin shirin za a ji cewa gwamnatin Tarayyar Najeriya ta saka kungiyar IPOB ta masu rajin kafa Biafra a matsayin kungiyar 'yan ta'adda. Ofishin ministan tsaron kasar ne ya sanar da labarin bayan arangamar da aka yi tsakanin sojojin Najeriya da 'yan kungiyar a Kudu maso gabashin kasar.