Cikin shirin za aji wasu da ake zargin 'yan kungiyar Boko Haram ne sun kashe mutane hudu tare da sace wasu biyu a Jamhuriyar Kamaru, a wasu hare-hare cikin dare da suka kai yankin arewa mai nisa. Bayanai sun ce uku daga cikin mutanen da aka halaka sun yi masu yanakn rago ne a garin Kolofata da ke kan iyaka da Najeriya.