Cikin shirin za a ji kamfanin Mai a Najeriya ya ce an sace masa ma'aikata 10 dake gudanar da aikin binciken Mai a jihar Borno a arewa maso gabashin kasar. Ana dai zargin mayakan kungiyar Boko Haram ne da yin awon gaba da masanan da suka shafe shekaru suna bincike kan albarkatun na Mai a yankin tafkin Chadi.