1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shirin kafa gwamnati a palasdinu

Zainab A MohammadMarch 16, 2006
https://p.dw.com/p/Bu7Q

MIDEAST

A yau ne ake kyautata zaton cewa,Kungiyar masu tsattsauran raayi na Hamas zata amince da batun nadin sabuwar gwamnati a yankin palasdinu,Sai dai bisa dukkan alamu tsohuwar jammiyar mulki ta fata bazata kasance cikin wannan gwamnati ba.

Kakakin yan Hamas dake yankin Salah al-Bardawil ya fadawa manema labaru hakan ayau ,bisa ga umurnin shugaba Mahmud Abbas,Abu mazen.Yace tun a daren jiya ne suka mikawa sauran kungiyoyi sabbin sauye sauye da aka samu.kuma an saurararon martaninsu a yau.

Ya kara dacewa idan sun amince da shiga gwamnatin hadakan,saanan zaa rarraba mukaman ministoci.

Majiysar yan Hamas din dai na nuni dacewa a yau ne kungiyar take jiran sakamakon tattauznawa na karshe dake gudana tsakanin shugabannin jammiyun siyasar yankin.